Aminu Adam Assalafiy
Munafar mu hadinkan musulmai abisa qur'ani da hadisi da maganganun magabata na qwarai.
MASOYIN MANZON (S) ALLAH NE KUMA AƘIDARSA TA SUNNAH CE
Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz D/ tashi jajirtaccen Malami ne mai ƙarfin zuciya da ƙwazo wajen koyar da Sunnah a tsahon lokaci ba tare da shakka ko nuna gajiyawa ba
Baya yin kāra ko kawaici wajen yiwa Bidi'a da ƴan Bidi'a martani, kusan bashi da na Biyu a cikin Dattijan Malaman Sunnah a wannan fanni.
Dr ya zama ƙarfen ƙafa ga ƴan Bidi'a manyansu da ƙananan su domin yadda ya hana su sakat ya sanya masu matuƙar ƙinsa, don haka basa yin wasa da duk wata dama da s**a samu ta yin ɓatanci gareshi.
A ranar Juma'a data gabata, Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz yayi bayanin tabbatar da Aƙidar Ahlussunnah dake tabbatar da cewa "BABU MAI TAIMAKO SAI ALLAH" cikin irin taimakon da Allah (swa) ne kaɗai yake iya bayarwa.
Babu Shakka wannan Aƙida ce tabbatacciya a Alkur'ani da Sunnah, a ƙoƙarin Dr na iyar da saƙon wannan Aƙida sai Kalmar
"Mai taimako shine Allah bamu son taimakon Inyasi, bamu son taimakon Tijjani, bamu son taimakon Abdulƙadiri, bamu son taimakon Shehu Usmanu
kai TAIMAKON MANZON ALLAH MA BAMU SON TAIMAKON SA
taimakon wa muke so..Allah...."
ta gangaro daga bakin sa, saidai ina rantsuwa da zatin Allah cewa:
Dr Idris Abdul-Aziz bai yi wannan lafazi da nufin yin rashin ladabi ga Annabi saw ba! Har maƙiyin sa yasan wannan.
Nufin Dr bai wuce tabbar da abinda ya koro a siyaƙin zancensa ba na cewa "Babu mai yin taimako sai Allah"
Ma'ana:
Annabi saw baya taimako, Shehu Inyass da Tijjani da Shehu Abdulƙadir da Shehu Usmanu basa yin taimako. Mai yin taimako Ɗaya ne tal, shine Allah (swa).
Saidai mun so ace Dr yayi amfani da Uslubi wanda ya ɗara wancan da yayi amfani dashi kyau da cika, ba don abinda ya faɗa kuskure bane, a'a cin bākin a Uslubin iyar da zancen ne ba a Aƙidar ba
Aƙidar kuma itace Asali, ba Usulubin iyar da karatun Aƙidar ba.
Allah yaƙi yarda cika ta tabbata ga kowa sai kansa kaɗai (swa) k**ar yadda bai sanya rigar Isma ga kowa ba sai ga Annabawansa masu girma.
Adalci shine karɓar ita waccan nag
Allah yabada lada
لقد لقيت فتاة اسمها مريم ،سرقت قلبي بسحرها، وبنظراتها الجميلة.
قال أبو سليمان الداراني رحمه الله:
من كان يومه مثل أمسه فهو في نقصــان.
شيخ الإسلام ابن تيمية رحمه الله .
((لا عيبَ على من أظهر مذهب السلف، وانتسب إليه، واعتزى إليه؛ بل يجب قَبول ذلك منه اتفاقا؛ فإن مذهب السلف لا يكون إلا حقا )) (كتاب التحفة المهدية لمن سأل عن معنى السلفية .
Salafiyya hanyar tsira
👇
kabi tafarkin salaf kasamu shiriya duk wanda yasa6a wa tafarkin salaf bazai samu shiriya ba dan haka
اتباع السلف
shi ake kira da salafiyya wato masu bin manhaji ko tafarkin salaf magabata nagari
👇
tambaya
suwaye ake kira salafus salih
من هم السلف الصالح ومن هم السلف هذه الأمة ؟؟
suwaye ake Kira salafus salih kumwa suwaye salaf din wannan Al'ummah tamu ??
👇
فالمراد باالسلف عند علماء الشرعي هم الصحابة والتابعون وتابعوهم بإحسان من القرون المفضلة هؤلاء هم السلف الصالح وهم سلف هذه الأمة
ma'anar salaf awajen malaman shari'ah sune sahabban annabi saw da tabi'ai da tabi'uttăbi'in wadanda s**a biyo bayãn sahabbai da kyautatawa wadannan sune magabata na gari kuma sune ake Kira salaf na wannan Al'ummah tamu
👇
وهم الذين قال رسول الله صلى الله عليه وسلم في شأنهم خير أمتي قرني ثم الذين يلونهم ثم الذين يلونهم
salaf magabata nagari sune wadanda annabi saw yafada cewa mafi alkairin Al'ummata sune qarni na wadanda narayu tare dasu sune sahabbai sannan wadanda s**azo bayansu sune tabi,ai sannan sai wadanda s**azo bayansu sune tabi'uttăbi'in
👇
قال الله سبحانه وتعالى في سورة النساء ومن يشاقق الرسول من بعد ما تبين له الهدى ويتبع غير سبيل المؤمنين نوله ما تولى ونصله جهنم وسآئت مصيرا
Allah ta'ala yafada cikin suratu nisa,i yace duk wan da yayi jayayya da annabi saw yaraba hanya da annabi saw bayan kuma shiriya tabayya na gareshi cewa annabi saw gaskiya ne dan sako ne daka wajen Allah swt sannan kuma yabi tafarkin da ba namummunai ba yakaucewa tafarkin masu imani Allah yace zamu ji6inta masa abunda yaji6intawa kansa sannan kuma makomarsa itace jahannama tir da mummunar makoma
👇
idan mai karatu yayi duba zuwaga wannan taqaitaccen bayani zai fahimci cewa
👇
فكل من كان على منهاج الصحابة والتابعين وتابعوهم باحسان فهو سلفي
ma,anar salafiyya shine bin manhaji ko tafarkin salaf wato magabata nagari sune wadanda mukayi bayaninsu acan sama kenan duk wanda yake jingina da,awarsa zuwaga tafarkin wadannan bayin Allah shine ake kira basalafe ko dan salafiyya
LAMARIN AKWAI KULLE KAI!!!
Yanzu a cikin irin wannan matsin da tsadar man fetur ne ake so mutane wasu su tashi su tafi jahohinsu domin jefa ƙuri'a???!!!
Abun akwai matuƙar ɗaure kai a ce kawo yanzu gwamnati ta kasa shawo kan wannan matsala.
Allah ka bamu shugabanni nagari.
Allah ka yafe mana.
✍️ UMAR SHEHU ZARIA
16 Rajab, 1444
(07/02/2023).
https://www.facebook.com/profile.php?id=100084753761468
Aminu Adam Assalafiy Munafar mu hadinkan musulmai abisa qur'ani da hadisi da maganganun magabata na qwarai.
نكرم طلاب النحو والصرف،
فاطلبهما يا اخي ولا تكن من الغافلين،
لأنه زين العالم المتفنن.
KE ƊIN NAN KI YARDA KE MAI TSADA CE A ADDININ MUSULUNCI❤️
Daga taskar Shaikha Zainab Ja'afar Mahmud
Mace a addinin Musulunci a matsayin ta na UWA Allah Maɗaukakin sarki ya bata gata na musamman domin ya sanya yi mata biyayya da ƙyautayi a gareta hanya ce da zata gadarwa da mutum zuwa Aljanna ko samun Aljanns madaukakiya .......
KE ƊIN NAN a matsayin ki na 'ya bai yarda a tozarta kiba ko a wulakanta kiba ko wofantar dake ba,
Ballama ya sanya cewa kula dake da tarbiyantar ki da ɗauke buƙatun ki da aurar dake a hannun nagartancen namiji dalili ne da zai gadarwa da wanda da yayi wannan aiki samun Aljanna
Domin Manzon Allah
S A W yace duk wanda ya kula da ya'ya mata guda biyu ya dauke bukatun su da larurorin su ya tarbiyyartar dasu zasu zamto mishi kariya daga wutar jahannama ranar gome kiyama
KE ƊIN NAN addinin ya sanya ki a matsayin ƴar uwa da za'a kula da ita a sa'ilin da akace babu uba a raye,
Ba'a yadda ki tsaya ki rasa inda zaki sa kanki ba,
Ba'a yarda ki fita kije kiyi aikin karfi da kwanji da wahala ki nemo kici ba sai a ka sanya ragamar ki ajikin dan uwan ki namiji wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya ɗora mai wannan nauyi kuma zai tambaye shi akan shi ranar gobe ƙiyama
KE a matsayin ki na matar aure addinin musulunci ya sanya kulawa dake da ɗauke Miki nauye nauye da wahalallu na rayuwar ki a matsayin dole a wuyan wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya sanya a matsayin abokin rayuwar kine ko mijin ki ne
Allah maɗaukakin sarki yace لينفق ذوسعة من سعته
Kowa zaiyi ne gwargwadon hali da yassarewar da abin hannun da Allah Maɗaukakin Sarki ya bashi
Mu'amala ma ba'a yarda ayi Miki bisa muzanci ba,
Allah Madaukakin Sarki yace وعاشروهن بالمعروف
KE ƊIN NAN Ni Maryam Ayagi ina baki shawara ki nemi wannan Muhadaha da Malama Zainab Ja'afar tayi saboda kiji tagomashin da gatan da addinin Musulunci yai Miki da babu wani addini da yayiwa ƴa mace irin wannan gata
A karshe ina rokon Allah sakawa Malama da Alkhairy ya kara mata Albarkaaa ikhlasi da ilimi mai Albarka.
✍️ Qs Ibraheem Sagir Zaria.
Jifan Shugaba kasa da duwatsu ba daidai bane, zagin sa ma ba daidai bane domin duk Wannan alama ce ta rashin tarbiya wanda shima zai iya jefa mu cikin masifa.
Daga sheikh bashir bello assalafiy Zaria.
NIGERIA TA ƊAUKI ZAFI
Matasa kar wani ya zuga ku, ku fito zanga-zanga ko bore ga shugabanni ko jami'an tsaro domin haka ba zai haifar da ɗa mai ido ba.
Sannan shugabanninmu yana da kyau su sani akwai rayuwa bayan mutuwa sannan ba koda yaushe ake amfani da karfi a mulki ba, lallashi ma salo ne mai kyau na shugabanci idan bukata ta k**a.
Allah ka bamu shugabanni nagari zaɓi daga gare ka ba zaɓi daga gare mu ba.
Haza wa salam.
✍️ UMAR SHEHU ZARIA
03 Rajab, 1444
(25/01/2023).
*"HIJABI"*
*Sheikh Ahmad Tijjani Guruntum*
_“Matar ka ta saka hijabi doka ne na Allah. Baka da hurumi akan saka hijabin ta. Dole ta saka hijabi, dole ta saka hijabi. Dole ƴarka ta saka hijabi, dole ƴarka ta saka hijabi. Babu zaɓi. Wannan Ubangiji_ _ne Yayi hukunci akan haka.”_
يَا *_أَيُّهَا النَّبِيُّ قُلْ لِأَزْوَاجِكَ وَبَنَاتِكَ وَنِسَاءِ الْمُؤْمِنِينَ يُدْنِينَ عَلَيْهِنَّ مِنْ جَلَابِيبِهِنَّ ۚ ذَٰلِكَ أَدْنَىٰ أَنْ يُعْرَفْنَ فَلَا يُؤْذَيْنَ ۗ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمً_ ا*
👏🏼👏🏼
السلام عليكم ورحمة الله وبركاته
Click here to claim your Sponsored Listing.
Videos (show all)
Category
Contact the business
Telephone
Website
Address
Kano
081287
Nomansland Kano
Kano
Makeup is a beautiful thing�� please let’s try to always look good at all time���
Burget Rimin Kebe
Kano
Muna dinkunah nazamnni masu kyau dogayan riguna hijab dinkin atamfa lace dasauransu located kano