Dr. Bashir Islamic Medicine Center

Munbude wannan shafi ne don taimakawa al'uma da magunguna. Lambar waya 08162600700 Lambar wayar Mallam 08162600700. Kano Nigeria.

Dr. Bashir mai rukiyyah da bayar da magunguna na musulunci dana gargajiya da addu'o'i da kuma shawarwari bisa kowace irin cuta.

Photos from Dr. Bashir Islamic Medicine Center's post 09/01/2024

SARIQUL JINNI سارق الجن

`Barawon Aljani.

Aljanu masu satar kayan mutane.

Galibin wadannan Aljanu a gidajen mutane suke zaune da kuma kasuwanni.

Suna iya satarwa mutane kudi, abinci da kuma sauran kayan amfani.

Waddannan Aljanu wato Sariqul Jinni s**an iya sato kayan mutane su kawo gidanka su ajjiye ko su ajjiye a aljihun mutum ko cikin kayansa.

Sannan suna aron kayan mutane daga baya su dawo musu da shi.

Sariqul Jinni suna da hadari sosai domin suna hada gaba da zargi a tsakanin mutane.

Hakanan suna da taurin kai sosai, ba sa rabuwa da mutum ko gidan mutane ta dadi.

Irin wadannan Aljanu su ne Bokaye masu buga kudi suke yin amfani da su ta hanyar saka su su sato musu kudaden jama'a.

Ashararain mutane suna iya yin Sihiri su tura Sariqul Jinni jikin wani mutum ko gidan wani mutum don su dinga satar masa dukiya suna 6atar masa.

Hakai dai Bokaye suna iya tura su jikin mutum, sai mutum ya zama tantirin 6arawo kuma yana yin satar ne ba a son ransa ba. Suna kuma iya shiga jikin mutum ta hanyar tsautsayi.

Sariqul Jinni sun dade a duniya. Domin Allah madaukakin Sarki ya yi bayani akan Aljanu masu satar ji a cikin Suratul Hijri da Suratus Saffati da Suratul Jinni da dai wasu surori na Alqur'ani.

SAHABIN MANZON ALLAH صلى الله عليه وسلم
YA K**A `BARAWON ALJANI

Aba Hurairata (RA) ya k**a Sariqul Jinni hannu da hannu.

An kar6o daga Aba Hurairata Allah ya kara yarda a gareshi, ya ce " Manzzon Allah صلى الله عليه وسلم
Ya wakiltani in kula da zakkar watan Azumin Ramadana. Sai ga wani ya zo yana satar abincin (da nake gadi).

Sai na k**a shi, na ce Sai na kai ka wajen Manzon Allah صلى الله عليه وسلم.

Sai ya ce min "WAllahi ni mabukaci ne kuma ina da iyali da yawa ga kuma tsananin bukata"

Sai na rabu da shi.

Da gari ya waye sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
Ya ce "Ya kukai da bakonka na jiya?"

Sai na ce Ya Ma'aikin Allah, ya koka min tsananin bukata da kuma yawan iyali. Sai na tausaya masa na kyale shi.

Sai Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
Ya ce "Karya yake kuma zai dawo"

Saboda haka sai nay tarkonsa.

Sai kuwa gashi ya dawo yana satar abincin. Sai na k**a shi, na ce to wAllahi sai na kai ka wajen Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
Domin karo uku kenan ina k**a ka. Se kay rantsuwa ba za ka dawo ba sai kuma ka dawo.

Sai ya ce "To ka kyale ni se in koya maka wasu kalmomi wadanda Allah zai sa ka amfana da su".

Sai na ce Wadanne ne?

Sai ya ce "Idan ka je wajen kwanciyarka, ka karanta Ayatal Kursiyyu har karshen ayar. To Akwai me gadi da Allah zai saka maka kuma Shaidan ba zai iya kusantarkaba har sai ka wayi gari".

(Da Manzon Allah صلى الله علي وسلم
Ya ji haka sai ya ce "Amma fa shi (wannan mai zuwar maka da daddaren) makaryaci ne, sai dai gaskiya ya gaya maka. Ya Aba Hurairata ka san ko da wa kake gamuwa har sau ukun nan?"

Sai na ce A'a.
Sai ya ce "Shaidan ne"

Daga wannan hadisi za mu fahimci cewa lallai Shaidanun Aljanu suna zuwa su saci kayan mutane.

YADDA MUTUM ZAI GANE SARIQUL JINNI YA SHAFE SHI.

Kalli bidiyoyinmu acikin wannan shuɗin rubutun
https://www.youtube.com/
Lambar waya 08162600700, 08134434846.

1- yawan 6atan kudi da kayan amfani kuma a rasa wanda ya dauka.

2- yanzunnan za ka ‘kirga kudi ka sa a aljihu ko wani abu amma in ka sake ‘kirgawa sai ka ga sun ragu.

3- duk irin 6oyewar da kay wa kudin ka sai ka ga an ta6a ma ka ko an dauke gaba daya.

4- zaka dinga yawan ganin an yi ma kaca-kaca dakayan ka, an yi ma bincike kuma ba ka san kowaye ba.

5- za ka ajjiye kayanka ko kudi sai ka ga an canja musu waje.

6- wani abinka zai 6ata, sai ka gaji da nema kaha‘kura sai kuma ka gan shi daga baya .

7- za ka ji kana da sha‘awar ka dauki kudin da bana ka ba ko wasu kaya koda kuwa ba abinda za kai da shi.

8- idan yaro yana da Sariqul jinni zai dinga yawan dauke-dauke kayan mutane da kudinsu kuma in an caje shi ba za a ga komai ba.

9- Za a dinga ganin yaro da kudi, in an tambaye shi a ina ya samu zai ce shi ma bai sani ba domin Aljanin ne ya sato ya saka masa.

10- Mai Sariqul jinni za a dinga yawan ‘kala masasatar da bai ji ba bai gani ba: don kuwa Aljanin nezai yi satar sai a ce kai ne.

11-Mutum zai ajjiye kudinsa amma sai ya tashi dauka sai ya ga sun zama takardu ko qasa ko kuma ganye.

SARIQUL JINNI TA HANYAR SIHIRI

Wani lokacin ana iya hada baki da Boka ya tura wa mutum Sariqul jinni don ya dinga yi ma sa 6arna acikin dukiyar sa.Shi kuma bayan alamomin da mu ka ambata asama to zai dinga fama da wadannan:-

1- karyewar kudin mutane a ka.

2- zai kasa kaya ai ta siyan na kowa amma a ‘kikallon na sa (don kuwa Aljanin ne zai lullu6e ma kayan ba wanda zai gan su)

3- ta6ar6arewar harkar ciniki.

4- kudi za su lalace amma ka rasa abinda ka siya dasu.

5- fama da matsanancin ciwon kai musamman dab da Magriba.

6-yawan faduwar gaba.

7- 6acin rai mara dalili.

7- za ka dinga mafarkin ana bin ka a guje ko anakokawa da kai.

8- za ka ji sam ba ka son fita kasuwa.

9- in kana kasuwa sai hankalin ka yai ta tashi,amma da ka dawo gida ko ka tafi wani wajen shikenan sai ka dena.

10-fada da abokan ciniki

11- za ka ji k**ar ana kiran sunan ka amma ba kaga kowa ba.

12- ko wani ka ba wa kudi indai na ka ne sai an yima sa sata.

Daga shafin Bashir Halilu mai Rukiyyah da bayarda magunguna na Musulunci dana gargajiya. Lambar waya 08162600700, 08134434846.

Kalli bidiyoyinmu acikin wannan shudin rubutun
https://www.youtube.com/

Photos from Dr. Bashir Islamic Medicine Center's post 05/01/2024

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ambaci Shaiɗanu Magina acikin Alqur'ani mai girma, cikin suratu Sad, ayah ta 37.

وَالشَّيَاطِينَ كُلَّ بَنَّاءٍ وَغَوَّاصٍ
Ga link na shafinmu na youtube, wanda za ku samu bidiyoyinmu

https://www.youtube.com/

03/01/2024

YADDA ALJANU SUKE HAWA SAMA DOMIN SATO MAGANAR MALA'IKU

https://www.youtube.com/

A cikin Alqur'ani mai tsarki, Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi magana akan masu hawa sama ko ƙoƙarin hawa sama, domin su saurari irin maganganu da Mala'iku suke yi, don su dawo ƙasa su dinga sanar da Bokaye da kuma yadda Allah Maɗaukaki Ya tanadi wasu taurari a sama masu jefe irin waɗannan Shaiɗanun masu yiwa Mala'iku laɓe.

Ka duba tafsirin Aya ta 23 cikin Suratu Saba'i da Ayah ta 7 cikin Suratus saffati da Ayah ta 18 cikin Suratul Hijri da dai wasu gurare da dama a Alƙur'ani, domin ganin yadda Allah Mai girma da ɗaukaka Yai bayani akan satar bayani da wasu Shaiɗanu suke yi daga Mala'iku domin su sanar da Bokayae, su kuma Bokaye su dinga taƙamar cewa sun san gaibu.

Yanzu ga wani Hadisi wanda bayani ya zo daga bakin Manzon Allah (SAW) game da yadda Aljanu suke hawa sama domin satar maganar Mala'iku da kuma abinda ya ke kasancewa.

روى البخاري عن أبي هريرة رضي الله عنه عن النبي صلى الله عليه وسلم قال:

إذا قضى الله الأمر في السماء ضربت الملائكة بأجنحتها خضعاناً لقوله، كأنه سلسلة على صفوان ينفذهم ذلك. حتى إذا فُزِّع عن قلوبهم قالوا: ماذا قال ربكم؟ قالوا: الحق وهو العلي الكبير فيسمعها مسترق السمع ـ ومسترق السمع هكذا بعضه فوق بعض ـ وصفه سفيان بكفه فحرفها وبدد بين أصابعه ـ فيسمع الكلمة فيلقيها إلى من تحته، ثم يلقيها الآخر إلى من تحته، حتى يلقيها عن لسان الساحر أو الكاهن فربما أدركه الشهاب قبل أن يلقيها، وربما ألقاها قبل أن يدركه، فيكذب معها مائة كذبة فيقال: أليس قد قال لنا يوم كذا وكذا: كذا وكذا فيصدق بتلك الكلمة التي سمعت من السماء.
صحيح.

Daga shafin Bashir Halilu mai Ruq'yah da bayarda magunguna na musulunci da na gargajiya. Lambar waya 08162600700, 08134434846.
Kalli cikakken wannan bayani acikin bidiyo acikin wannan shuɗin rubutun
https://www.youtube.com/.
Wannan hadisi ya zo da ruwayoyi daban-daban amma za mu yi bayanin ma'anarsa tare da shigar da bayanin sauran ruwayoyin acikin fassarar.

Acikin wannan sahihin Hadisi da Bukhari ya ruwaito, Manzon Allah SallAllahu alaihi wa sallama ya ce

"Idan Allah Ta'ala Ya yanke wani hukunci a sama, wato acikin fadarsa, sai sama ta k**a girgiza mai ƙarfi ko ko kuma tsawa mai ƙarfi, sai kuma Mala'iku su dinga bubbuga fuka-fukansu, don nuna girmamawa ga umarnin Allah Maɗaukakin Sarki, kai ka ce sarƙa ake bugawa akan fan dutse kuma su faɗi suyi sujjada. Har sai sun samu nutsuwa tukuna, sai ya zamanto Mala'ika Jibrilu shi zai fara ɗago kansa, sai Allah Maɗaukakin Sarki Ya sanar da shi abinda ya nufa. Daga nan sai sauran Mala'iku su dinga cewa "Me Ubangijinmu ya ce ya Jibrilu?". (Ma'ana wane umarni Allah Ya bayar?). Sai ya ce "Allah Ya yi umarni na gaskiya ne, kuma shi ne Maɗaukaki mai girma.
Dukkan saman da Mala'ika Jibrilu ya wuce sai Mala'iku su ce masa" "Me Ubangijinmu ya ce Ya Jibrilu? ". Shi kuma sai ya ce gaya musu abinda Allah Ya sanar da shi.

Sai Mala'iku su dinga gayawa ƴan uwansu Mala'iku cewa Allah Ya ce za a yi kaza da kaza a duniya. Suna cikin wannan magana ne sai Aljanu masu sauraron maganar Mala'iku su ji wannan zance da Mala'iku suke yi, sai Aljanin da ke can kusa da sama ya gayawa Aljanin da ke ƙasansa abinda ya ji, shi ma ya gayawa na ƙasansa. Kowane in ya tashi sai ya ƙara ƙarya ɗari cikin abinda ya ji, sannan ya gayawa na ƙasa da shi. Sun kasance suna hawa sama ta hanyar wani ya taka kafaɗar wani, shi ma wani ya hau kan kafarsa har izuwa sama. Haka za su yi ta gayawa junansu wannan magana da su ka jiyo daga sama, har zuwa na ƙasansu, wanda shi kuma zai je ya gayawa Boka cewa abu kaza zai faru a duniya rana kaza a waje kaza. To wani sa'in Aljanin ya kan samu dama ya faɗawa ɗan uwansa zancen da ya jiyo, wani sa'in kuma kafin ya faɗa sai tauraro ya jefe shi, ya kashe shi.
To daga nan sai Bokan ya dinga gayawa mutane cewa abu kaza zai faru rana kaza, sai kuma a ga abun ya faru. Sai ka ji mutane suna cewa 'Ai rannan ya ce da mu abu kaza zai faru, kuma abun ya faru da gaske'. Sai su dinga gasgata shi saboda wannan kalma da aka jiyo daga bakin Mala'iku a sama.
Bukhari ne ya ruwaito shi, wasu sassansa kuma daga wasu Malaman ne.

https://www.youtube.com/

Acikin wanna ƙissa za mu fahimci cewa

1) Aljanu suna iya zuwa wani waje mai nisan gaske acikin sararin samaniya, ta yadda suke iya jin maganganun da Mala'iku suke tattaunawa akan abubuwan da za su faru a duniya.

2) Aljanu ba sa iya tunkarar Mala'iku domin su samo labarin abinda zai faru a duniya, sai dai suyi masu laɓe, su sato wata kalma ba tare da Mala'ikun sun sani ba.

3) Aljanu da Mala'iku dukkansu ba su san gaibu ba, har sai Allah Ya kira Mala'ika Jibrilu Ya sanar da shi, sannan su sani.

4) Aljanu suna iya kaiwa inda za su ji maganar Mala'iku ne ta hanyar taka kafaɗun junansu, wannan ya hau kan wannan, wannan ya hau kan wannan, har su isa zuwa sama.

5) Ba kowane lokaci ne Aljanu suke samun damar satar maganar Mala'iku ba, domin wani lokacin tauraro yana jifansu, ya kashe su kafin su kawo zancen zuwa duniya.

6) Ainihin maganar da Aljanu su ka jiyo a sama ba ita suke kawowa ƙasa ba, sai sun ƙara ƙarerayinsu aciki sannan su kawowa Boka, shi ma ya ƙara ƙaryarsa sannan ya sanar da mutanensa.

7) Abinda Bokaye suke gayawa mutane yawanci ƙarya ne, sama da 99% ƙarya ne, sauran kuma irin maganar da aka sato daga Mala'iku ce, sai ka ga sun faɗi abu kuma ya faru. Shi ne dalilin da ya sa wasu suke gasgata Bokaye.



8) Malamai sun yi bayanin cewa ba kowace magana ce ake barin Aljanu su jiyo ta daga sama ba, misali wahayin da ake kaiwa Annabawa, ba a bari wani Aljani ya san da wannan magana kafin ta je ga Annabin Allah.

Kalli cikakken wannan bayani acikin bidiyo acikin wannan shuɗin rubutun
https://www.youtube.com/.

Daga shafin Bashir Halilu mai Ruq'yah da bayarda magunguna na musulunci da na gargajiya. Lambar waya 08162600700, 08134434846.

24/12/2023

AYATUSH SHUFA'I

بِسْمِ اللّٰهِ الرَّحْمَـٰنِ الرَّحِيمِ
• « قَاتِلُوهُمْ يُعَذِّبْهُمُ اللَّهُ بِأَيْدِيكُمْ وَيُخْزِهِمْ وَيَنْصُرْكُمْ عَلَيْهِمْ وَيَشْفِ صُدُورَ قَوْمٍ مُؤْمِنِينَ» الآية 14 من سورة التوبة.

• «وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ» الآية 80 من سورة الشعراء.

• « يَا أَيُّهَا النَّاسُ قَدْ جَاءَتْكُمْ مَوْعِظَةٌ مِنْ رَبِّكُمْ وَشِفَاءٌ لِمَا فِي الصُّدُورِ وَهُدًى وَرَحْمَةٌ لِلْمُؤْمِنِينَ » الآية 57 من سورة يونس.

• « ثُمَّ كُلِي مِنْ كُلِّ الثَّمَرَاتِ فَاسْلُكِي سُبُلَ رَبِّكِ ذُلُلًا يَخْرُجُ مِنْ بُطُونِهَا شَرَابٌ مُخْتَلِفٌ أَلْوَانُهُ فِيهِ شِفَاءٌ لِلنَّاسِ إِنَّ فِي ذَلِكَ لَآيَةً لِقَوْمٍ يَتَفَكَّرُونَ » الآية 69 من سورة النحل.

• « وَنُنَزِّلُ مِنَ الْقُرْآنِ مَا هُوَ شِفَاءٌ وَرَحْمَةٌ لِلْمُؤْمِنِينَ وَلَا يَزِيدُ الظَّالِمِينَ إِلَّا خَسَارًا » الآية 82 من سورة الإسراء.

• « وَلَوْ جَعَلْنَاهُ قُرْآنًا أَعْجَمِيًّا لَقَالُوا لَوْلَا فُصِّلَتْ آيَاتُهُ أَأَعْجَمِيٌّ وَعَرَبِيٌّ قُلْ هُوَ لِلَّذِينَ آمَنُوا هُدًى وَشِفَاءٌ وَالَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ فِي آذَانِهِمْ وَقْرٌ وَهُوَ عَلَيْهِمْ عَمًى أُولَئِكَ يُنَادَوْنَ مِنْ مَكَانٍ بَعِيدٍ » الآية 44 من سورة فصلت.

22/12/2023

AMFANIN ZA'AFARAN DA AMBAR DA KUMA ALMISKI WAJEN KYAUTATA LAFIYA.

Daga Shafin Sunnah Medicine, masu yin Ruq'yah da harhada Magunguna na Musulunci. Lambar waya 08162600700.

1) ZA'AFRAN.
Shi Za'afaran wata ciyawa ce ko kuma tsiro mai dauke da launi mai abin sha'awa, galibi jar ciyawa ce ko yaluwa. Da akwai man Za'afran, da akwai turarensa kuma ana samun ciyawar tasa ma.
Ana amfani da shi wajen sinadarin girki kuma yana maganin cututtuka da dama yana kuma kyautata lafiya.

An fara noman Za'afaran ne a wajejen Greece. Sannan akay Safararsa zuwa Yammacin Amurka da kuma kasashenmu na Afrika.

Za'afaran yana maganin cututtuka k**ar:

★Zubewar Gashi.
Shafa Man Za'afaran a fatar kai yana maganin sanqo. Hada Za'afaran da madara a shafa a kai yana maganin zubewar gashi kuma yana kara yawan gashi.

★Gyaran Fuska
Hada Za'afaran da madara a shafa a fuska a hankali amma a kaucewa ido. A bar shi tsawon minti goma sha biyar sannan a wanke da ruwa yana sa fuska tay kyau da sheqi. Ana yin wannan hadin sau daya a sati.

★Matsalolin fata.
A jika ciyawar Za'afaran a ruwa tsawon awa biyu zuwa uku. Sai a shafe fatar jiki da shi. Yana bada fata mai laushi da taushi. Ana yin haka sau biyu zuwa uku a sati.

★Maganin kuraje.
A hada Za'afaran da Ray'han a kir6a a shafa akan fata sai a wanke bayan minti goma. Wannan hadin yana maganin kuraje, kyasbi, makero da tabo da kuma sauran cututtukan fata.

★Kwayoyin Cuta.
Zuba ko fesa Za'afaran a waje yana maganin kwayoyin cututtuka da ba'a iya ganinsu kuma yana kyautata lafiya.

★Kyautata Bugun Zuciya.
Za'afaran yana da sinadarin potassium wanda ke kyautata bugawar zuciya da kuma bata damar yin aikinta yadda ya k**ata.

★Zagayawar jini.
Za'afaran yana da sinadarai irinsu coper, potassaium, calcium, manganese, iron, magnesium, da zinc da kuma selenium. Wasu daga cikin wadannan sinadarai suna taimakawa wajen daidaita yanayin jini a jikin mutum.

★Rigakafin Cutar Kansa (cancer).
Za'afaran yana dauke da wasu kananan sinadarai k**ar zea-xanthin da lycopene wadanda ke kare jikin mutum daga kamuwa da cutar Kansa wato Daji.

★Saukaka Narkewar Abinci.
Za'afaran yana da muhimmanci wajen saukake narkewar abinci a jikin mutum saboda sinadarin anti-cinvulsant da sauran sinadarai dake cikinsa.

★Ciwon Hakori.
Shafa Za'afaran hade da Zuma yana taimakawa wajen maganin cututtukan dasashi da hakori.

★Cututtukan Cikin Baki.
Idan aka hada Za'afaran da Zuma da Graceline ana shafawa a cikin baki yana maganin kuraje da sauran cututtukan da kan iya samuwa a cikin baki.

★Gyaran le6e.
Za'afaran yana cikin tsirrai kadan wadanda ke samar da sinadarin vitamin B2 mai yawa. Amfani da shi yana gyara la66a da kuma kyautata hadiyar abinci daga baki zuwa makogwaro.

★Maganin Sanyi da Tari.
Idan aka hada Za'afaran 1grm da ruwa 1ltr aka sha yana maganin Sanyi da kuma Tari.

★Jini lokacin Al'ada.
Za'afaran yana da kyau wajen daidaita zuwan jini yayin al'ada.

★Maganin Maza.
Amfani da Za'afaran yana taimakawa mazaje su dawo da karfinsu. Hatta tsofaffi yana ba su kuzari sosai.

★Maganin Aljanu da Sihiri.
Hada Za'afran da Jan Almiski da Ambar, a dinga shafawa a fata, yana maganin cututtukan Aljanu kuma yana taimaka wajen 6ata sihiri da ke jikin mutum.

★ Amma a kula ★

☆Yin amfani da Za'afaran ba bisa ka'ida ba zai iya sawa mutum:-

* Mura
*Ciwon Kai
da kuma
*Daukewar Miyau a baki.

★ Masana harkar lafiya ba suy bayanin illar Za'afaran ga mace mai ciki ba, sun ma dai ce yana taimaka mata.

Daga shafin Sunnah Medicine, Masu yin Ruq'yah da harhada Magunguna na Musulunci. Lambar waya 08162600700.

2)AMFANIN AMBAR GA LAFIYAR AL'UMA.

Ambar wani magani ne da ake samun sa daga jikin wata bishiya. Wato k**ar irin farin ruwan nan dake fita daga jikin bishiya. Shi ne ake hada
shi da wasu sinadarai a samar da Ambar. Kuma ana samunsa a jikin bishiyoyi da dama. Idan ku ka duba wannan hoton za ku ga hoton Ambar k**ar Qaro.

Bayan amfanin da Ambar yake da shi wajen kiwon lafiya, haka ma yana taimakawa wajen magance cututtukan jiki da na jinnu ko sihiri.

Ana iya hada Ambar da wasu magunguna k**ar zuma, miski, habba, zaitun, da dai sauransu, ayi amfani da shi don samun ingantacciyar lafiya

Yi amfani da Ambar kadan ka samu lafiya mai yawa da yaddar Allah.

Ana samun Anbar na gari, ana samun na ruwa, ana samun na turare, ana
samun kwa6a66e na shafawa .

★ Sanya nishadi.
Ambar yana sanya nishadi idan aka sha kilogram daya tare da zuma cokali daya.

★Kara karfin hakora.
Ambar yana kara karfin hakori idan ana goge hakora da man sa, wato Amber oil.

★Gyara kwakwalwa.
Man Ambar yana maganin cututtukan kwakwalwa idan ana shan sa tare da Man zaitun
da Habbatussaudaa.

★Maganin ciwon Hauka.
Ga mai lalurar hauka sai adinga tofa ayoyin Ruq'yah a cikin Ambar, a zuba a ruwa, a ba shi, ya sha kuma a dinga yi masa hayaki da shi musamman a
hada da miski wajen hayakin.

★Ciwon kai.
Ciwon kai bari guda sai a hada Ambar da jan miski da Man juda a kwa6a, a dinga shafawa a kan kuma ana yin hayakin sa.

★Lalata sihiri.
Ana amfani da Ambar ta hanyoyi da dama wajen 6ata sihiri wanda mutum ya ci ko ya sha.

★Hawan jini.
Masu hawan jini su sha Ambar kadan a cikin ruwa.

★Gyaran fata.
Don gyaran fata da jin dadin jiki, sai a diga Ambar kadan a cikin ruwan wanka ay wanka da shi.

★Dadin bacci.
Mai son yin bacci mai dadi shi ma sai ya zuba Ambar kadan a ruwan wankansa.

★Hutawar kwakwalwa.
Ambar yana taimakawa kwakwalwa wajen samun hutu mai dadi.

★Lafiyar zuciya.
Amfani da Ambar yana kara kyautata karfin zuciya.

★Asthma.
Masu cutar Asthma su ma Ambar yana taimaka musu idan suna amfani da shi.

★Gudanawar jini.
Amfani da Ambar yana kara kyautata gudanawar jini a jikin mutum.

★Karfin jima'i.
Yin amfani da Ambar yana kuma kara karfin jima'i ga maza da mata.

★Narkewar abinci.
Amfani da Ambar na saukaka narkewar abinci a cikin ciki, yana hana kumburin ciki, tusa da sauran matsalolin ciki.

★Dadin jiki.
Yana kara soyayya tsakanin miji da mata, idan dayan su yana amfani da
shi.

★ Warkewar ciwo da kashe kwayoyin cuta.
Sai a zuba man Ambar a kan
ciwon bayan an wanke shi. To zai warke cikin sauki insha Allah.

★ Amma a kula ★
Duk da amfanin Ambar kuma zai iya cutarwa .

★Mata masu ciki su guji amfani da Ambar, musamman sha a ciki.

★Ambar din da ba a gauraya shi da wani abu ba k**ar ruwa da mak**antansu, to a guji shan sa kai tsaye.

★Ba'a sa Ambar a cikin ido.

★A guji ajjiye Ambar kusa da yara.

Daga cibiyar sunnah medicine, masu yin Ruq'yah da harhada Magunguna na Musulunci. Lambar waya 08162600700.

3) AMFANIN ALMISKI

Shi Miski ba tsiro ba ne, ana samar da shi ne daga jikin Barewa, kuma Allah ya fade shi a Alqur‘ani.

Amfanin sa.

★ Yana maganin dafi kowane iri.

★ Yana kara karfin jiki.

★ Yana maganin hawan jini idan an sheka.

★Yana maganin Aljanu, ya kan ma iya kashe Aljani idan an hada shi da Za‘afaran ana shafawa, ana kuma iya zuba shi a garwashi a dinga hayaki.

★Yana maganin warin gaba idan ana shafawa.

★Yana maganin namijin dare.

★Yana taimakawa masu matsalar haihuwa idan suna matsi da shi bayan gma al'ada.

Akwai jan Miski akwai baki kuma akwai farin Almiski akwai kuma miski na ruwa.

Daga cibiyar Sunnah Medicine, masu yin Ruq'yah da harhada Magunguna na Musulunci.

Lambar waya 08162600700.

04/12/2023

YADDA ZA KA MALLAKI AL-JANI YA DINGA YI MA KA AIKI.

A binciken da Shafin Sunnah Medicine ya gabatar, ya gano cewa, hanya daya cikin hudu mutum zai bi domin ya mallaki Aljani, ya dinga yi ma sa aiki.

Daga cibiyar Sunnah Medicine, masu yin Ruq'yah da harhada magunguna na Musulunci.

Shi ga cikin wannan shudin rubutun kayi downloading Application dinmu, wanda za ka dinga samun rubututtukanmu cikin sauki

https://appsgeyser.io/7550770/Bashir%20Halilu%20Tarbiyyah%20Islamiyyah

Lambar waya 08162600700.

بسم الله، والصلاة والسلام على رسول الله، وبعد:-

1)-Hanya ta farko ta mallakar Aljani ko Aljanu da yawa, ita ce mutum ya sadaukar da ruhinsa da gangar jikinsa ga Aljani domin ya dinga biya masa bukata.
Ita wannan hanya ta mallakar Aljani, ta fi kowacce hanya tsantsar kafurci da shirka. Ta yadda mutum zai amince cewa ya zama bawan Aljani kuma ya barranata kansa da Allah Mahaliccin halitta baki daya. Wannan hanya tana da hanyoyi daban-daban kusan guda bakwai, wadanda na ta6a kawo bayanin hanyoyin dalla-dalla kusan shekaru uku da s**a wuce. A takaice dai wasu daga cikinta su ne akwai:-
i) Dariqatuz zab'hi طريقة الذبح
wato hanyar yanka, ta yadda mutum zai dinga yankawa Aljanu wata dabba suna shan jininta. Kowa ya san duk wanda yay wa wanin Allah yanka to ya zama mushriki. Shiga wanna shudin rubutun domin karanta cikakken bayan akan hukuncin yanka wata dabba domin Aljanu
https://m.facebook.com/sunnahmedicinepage/photos/a.1374341292684795/2087353001383617/?type=3&source=54&ref=bookmarks
ii) - Akwai Dariqatul Tankiys طريقة التنكيس
Wato hanyar da mutum zai dinga wulakanta Alqur'ani ko kuma canja Alqur'ani daga ainihinsa. Misali a hada ayoyin Alqur'ani da sunayen wasu Shaidanu a dinga karantawa a tare ko a rubuta wata aya gaba-abaya ko kuma a rubuta Alqur'ani da jinin haila ko a saka shi acikin kazanta. Ya kuma hada da buda wasu haruffa na Alqur'ani a saka wasu sunaye aciki. Cikakken bayani dai akan wannan hanya yana nan acikin littafin 'Assarimul battar'.
iii) Sannan akwai hanyar da mutum zai dinga yin wata ibada ta musamman saboda Aljanu. Kamar ya ajjiye wani gunki, ya dinga yi masa sujjada. Wani za su saka masa sharadin ya dinga zama da janaba ko ya dena sallah ko karatun Alqur'ani. Daga cikin masu bin irin wannan hanya akwai wanda ko sallama ba ya amsawa, wani ma in zai baiwa mace magani to zai gaya mata cewa ta bari sai lokacun da take haila sannan ta zo, ko namiji ace lokacin da yake da najaba, sannan za a saurare shi.
iv) Daga cikin kazantar wannan hanya, akwai wanda Aljanu suke luwadi da shi da sauran ayyukan kazanta.
Da dai sauran hanyoyi da dama. Mai son karanta cikakken bayani akan ragowar hanyoyin sai ya duba rutun da nayi akan 'Siffofin Bokaye ko Yadda ake gane boka'.
To Boka ma'abocin wannan hanya ta farko, ma'ana 'Hanyar sadaukar da ruhi da gangar jiki ga Aljanu', ya fi saurin tara masifaffun Aljanu masu yawan gaske kuma 'yan bala'i. Yawancinsu ko kuma dukkansu arna ne marasa imani, wadanda ake saka su ayyukan kisa da sauran muggan laifuka.
Saidai Boka mai bin wannan hanya ya fi sauran bokaye shiga cikin hadari da sharrin Aljan. Domin aduk lokacin da ya sa6awa Aljanunsa to za su yanke masa hukuncin kisa ne ko su haukata shi, ko su kashe masa iyalansa ko su koma jikinsu. Haka nan daga cikin sharadan da suke sanyawa mai aiki da su shi ne, ba su yarda ya tuba ko ya dena aikin ba, haka nan ko ya mutu sai sun koma jikin 'ya'yansa sannan ba za su ta6a tashi daga gida ko wajen da yake aikin da su ba, komai tsawon shekaru. Domin kuwa sai ya amince ya gina musu mahalli na dindindin a wajen. In tafiya tay tafiya ma za su ce ba su yarda ya dinga kar6ar kudi ba ko kuma duk kudin da ya samu saidai ya kona ko ya rabawa mutane kuma dole ya bi su, don gudun fadawa masifarsu. Shi yasa za ka ga Boka a qungurmin daji ko acikin gida kwararra6a66e, 'ya'yansa da matayensa da shi kansa duk a cikin wahala da talauci, ga shi manyan attajirai suna zuwa suna kawo masa kudi, sai ka rasa yadda yakeyi da su. Kuma ko ya mutu 'ya'yansa ba abinda za su gada sai tarkacen kayan bokaanci da bakaken Aljanu, domin duk Aljanunsa sun sa ya lalatar da abinda ya samu.
Da dai matsaloli da yawa gaskiya. Duk bokan da ke bin wannan hanya karshensa mutuwar wulakanci, wasu malamanma sun ce ba ya cikawa da imani, ga shi duniyarma ba tay masa dadi ba.
Allah Ya tsare mu.

2)- Hanya ta biyu ta Mallakar Aljanu ita ce, a kafa kamfani tsakanin Aljani da mutum, duk ribar da aka samu sai a dinga rabawa, kowa ya dauki nasa.
Wannan hanyar itama akwai shirka acikinta da kuma tsabagen karya da yaudara ta fuskar Aljanun, kuma itama tana da hadari, saidai ba ta kai hanya ta farko ba amma dai dukkansu 6ata ne. Wato Aljanin zai dinga yiwa bokan aiki, in ya so duk kudin da bokan ya samu sai a raba, ya dauki nasa, ragowar kuma ya baiwa Aljanin. Wasu Aljanun suna kar6ar kudi cash, wasu kuma su ce ya siyo musu dabba su sha jininta, wasu su ce ya je gidan tururuwa ko cikin shuri, ya zuba kudin, wasu kuma su ce ya siyo musu bakaken kaya ko jajaye kodai wata kala da suke bukata. Akwai kuma wadanda za su cewa bokan ya tafi waje kaza, daidai lokaci kaza, zai ga wani mutum mai siffa kaza, sai ya ba shi kudin.
Bokan da ke bin wannan hanya, ya fi sauran bokaye saurin tara kudi na fitar hankali da samun daukaka da farin jini cikin kankanin lokaci sannan ya fi sauran bokaye yin abubuwan mamaki, k**ar ya dinga buga kudin jabu ko baiwa 6arayi sa'a da sauran abubuwan 'badali بدل' da tahriqul adat, k**ar ka ga mutum ya saki carbinsa kuma carbin ya tsaya a sama, bai fado ba. Nan da nan za ka ga mutum yana samun kudi yana gine-gine, yana hawa motoci.
Saidai kash, mabiya irin wannan hanya ba sa dadewa suna yi, da zarar mutane sun fara ganosu cewa macuta ne, sai samun kudinsu ya fara raguwa, daga nan sai Aljanun duk su gudu, su barsu, tunda kasuwancin ya fara samun matsala. Sai kuma Mallam ya koma damfarar mutane da cin bashi, karshe ya fada talauci, duk ya siyar da abubuwan da ya tara, ya koma matalauci, har jama'a su dinga tausaya masa. Ma su bin irin wannan hanya yawanci ba sa karewa da mutane lafiya, domin akasarinsu bayan Aljanun sun barsu sai kuma asirinsu ya fara tonuwa, ka ga mutane suna kai su kotu da sunan sun ci kudinsu, sai ka ga saidai mutum yay hijira ko ya kare a kurkuku. Mutane da yawa shaida ne akan yadda ta ke karewa da shahararrun bokaye.
Aljanu masu wannan halayya ta kashe-mu-raba da bokaye, ba sa aiki da kowa sai matashi, mai ji da kuruciya, in ya fara tsufa ko kuma samun kudinsa ya ragu sai su hada shi rigima da mutane, su gudu, su bar shi.
Da dai matsaloli da yawa gaskiya.
Allah Ka raba mu da sharrin duniya.

3)- Hanyar Mallakar Aljani ta uku kuma ita ce - Mallakar Aljani ta karfin tsiya, tahanyar yin amfani da Sarakunan Aljanu ko kuma amfani da hanyoyin tsafi, ta yadda za a tsafe Aljanin, ya dinga yin aiki ala dole.
Hanyoyi ne guda biyu.
Ta farko wata hanya ce ta tsantsanta bauta ga wanin Allah, ta yadda mutum zai nemi taimakon Sarakunan Aljanu da neman kusanci a garesu ta hanyar allantar da su ko neman taimakonsu. Wato mutum zai kaskantar da kansa a garesu ta hanyar yin wuridin sunayensu ko amfani da wasu nau'ukan turaruka da suke bukata ko ziyartar mazaunansu da kuma neman su tallafa masa da hadiman Aljanu. Saidai Malamai sun ce, wannan hanyar itama, tsantsar kafurcin da ke cikinta k**ar hanya ta farko ce, domin sai mutum ya zama cikakken bawan shaidan kuma barranta kansa da Allah Madaukakin Sarki sannan suke amincewa da shi. To sai Sarkin Aljanu ya za6o wawaye acikin bayinsa ya mallakawa wannan mutumi, shi kenan sai ya cigaba da tasrifi da su. Duk Aljanin da ya sa6a masa kuma sai ya kai kararsa wajen Sarkin Aljanu, shi kuma ya hukunta shi.
`Bangare na biyu acikin wannan hanya ta Mallakar Aljanu kuma ita ce mutum ya mallaki Aljani ta hanyar tsafi da sihiri.
Misali, akwai mutanen da su ka iya danawa Aljani tarko k**ar yadda ake danawa 6era tarko kuma su k**a shi. Wasu s**an dana tarkon a makabarta wasu su dana a tsakiyar daji, lokacin da hasken farin wata ya kai daren sha hudu. Akwai dai hanyoyi da dama da ake bi domin a k**a Aljani a hannu, kuma wannan ba wani sabon abu bane, sananne ne a wajen kowa, domin har turawa ma suna yi. To masu amfani da wannan hanya, su kan k**a Aljanu da yawa, su ajjiyesu, ta yadda za su dinga saka su ayyuka masu wahala sannan Alajnun suna yi ala tilas.
Bokan da ke amfani da irin wannan hanya to in ya turawa mutum Aljani gaskiya ba karamar wahala ake sha da shi ba. Irinsu za ka ji in an zo rukiyyah sai Aljanin ya ce shi ba zai fita ba, domin idan ya fita bokan ya ce sai ya kashe shi ko kuma zai kashe masa iyayensa. Wani Aljanin ma shi kansa bai san ta yadda akai bokan ya saka shi ajikin mutum ba kuma bai san ta yadda zai fita ba. Za ka samu suna matukar tsoron bokan domin gani suke k**ar shi ne allansu. Aljanu da yawa da suke jikin mutane ba a sin ransu suke zaune ba kuma inda sun san wata hanya da su bi su fita to da sun fita, musamman wadanda aka turosu ta wannan hanya.
Irin wannan bokan Aljanu suna matukar tsoronsa tare da yi masa biyayya kuma yana hukunta su ne ta hanyar dauri ko ya sa manyansu su azabtar da su, wani ma ya kan yankewa Aljani hukuncin kisa.
To amma fa mai amfani da wannan hanya, bayan kasancewarsa Boka, Mushriki kuma arne, to yana cikin hadarin gaske. Bokan da ke bin wannan hanya kusan ya fi dukkan bokayen duniya fuskantar barazana daga sharrin Aljanu, kuma ko da ransa ko bayan mutuwarsa sai Aljanu sun dau fansa akansa ko akan 'ya'yansa. Kasancewar yana tilasta musu suyi masa biyayya, sai hakan ta sa ya zama babu soyayya ko kauna ko amana kwata-kwata a tsakaninsu, suna matukar jin haushinsa da kuma fatan su samu wata dama da za su nuna masa shayi-ruwa ne. Don haka a duk lokacin da yay sake ko Allah Ya jarrabe shi, Aljanun su ka samu wata dama akansa, to kuwa za su kashe shi a take, ko su haukata shi ko su k**a iayalansa ko su hada masa gobara. Gaskiya irin wanna bokan shi kansa ba shi da kwanciyar hankali, domin zai ta fama da mafarkai masu abun tsoro da yawan firgita. Wani ma za ka ga yana ba da magungunan Aljanun amma shi kansa a firgice ya ke. Da za a yi masa ruqiyyah Allah ne kadai ya san Aljanun da za a cire masa.
Gaskiya dai wannan hanyar itama 6ata ce da kuma shirka. Allah Ya kiyaye mu.

4)- Hanyar mallakar Aljanu ta hudu kuma ta karshe, ita ce shi Aljanin da kansa ya bijirowa mutum, ya ce yana so ya dinga taimaka masa ko su dinga yin aiki tare.
Wannan ta kan faru ta hanyoyi daban-daban. Misali, idan mutum ba shi da lafiya yana matsalar Aljanu, sai ka ji Aljanun sun ce zai samu lafiya amma suna so ya dinga ba da magani, ma'ana su dinga taimaka masa, yana baiwa al'uma magunguna. Wani lokacin kuma idan kana ruqiyyah ko kana bada magungunan Aljanu, sai Aljanun su dinga zuwar ma ka, suna cewa suna so su taya ka ko su taimakeka akan aikinka. Na yi cikakken bayani akan 'Aljanu masu shiga jikin masu rukiyyah da masu nazari akan rayuwar Aljanu' za ka iya karanta cikakken bayanin acikin wannan shudin rubutun
https://www.facebook.com/Tarbiyyahislamiyyahislamichealthcenter/photos/a.431360137026800/754018684760942/?type=3
Wani mutumin kuma yana tafe a hanya ma zai gamu da su, su bayyana masa cewa suna so su taimaka masa, wani kuma amafarki suke zuwar masa da bayanin. Galibin irin wadannan Aljanu su kan nunawa mutum cewa su 'Rauhanay' ne ko musulman Aljanu kuma s**an nunawa mutum cewa ya dinga yawan ibada da sadaka da sauran ayyukan addini. Karanta cikakken bayani akan 'Su waye Rauhanay? ', acikin wannan shudin rubutun.
https://www.facebook.com/Tarbiyyahislamiyyahislamichealthcenter/photos/a.431360137026800/754018684760942/?type=3
Kamar yadda ka ga bayani, inda ka karanta abinda ke cikin wannan shudin rubutun, to yawancin wadannan Aljanu karya sukeyi, munafukai ne, wasu ma arna ne ba musulami bane, domin sai bayan ka amin ce da su sannan za ka gano hakan.
Irin wadannen nau'in Aljanu, sun fi shiga jikin mata, da kuma jahilan mutane. Za ka ji wata matar ta ce ta ga Annabi صلى الله عليه وسلم acikin dakinta, har ya ce ta dinga baiwa mutane magani, wata ta ce Nana Fadima ta bayyan a bangon dakinta, har da wafanda wasu Shehunai suke zuwa musu. Na ta6a dora muku videon wata mata, wacce ta ce Manzon Allah صلى الله عليه وسلم
yana zuwa wajenta, har yana hanata sallah da cin abinci kuma ya ce ta fito ta bayyanawa mutane cewa ita 'yarsa ce, har yanzu bidion yana nan a shafina na 'youtube', shiga wannan shudin rubutun ka kalleta kuma ka ji da bakinta.
https://youtu.be/d2qnRx3DTiY
Haka nan na ta6a dora muku hirarmu da wani Aljani, wanda yake zuwarwa wata yarinya, yana cewa shi ne Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم، har ya bata sadakar gashi, ya ce a dinga jikawa marasa lafiya. Shiga wannan shudin rubutun ka saurari hirarmu da Aljanin, ka ji yadda yake bayani da bakinsa.
https://clyp.it/user/xqrkhu2n
Sannan wadannan Aljanu, in s**a ga mutum mai kokarin ibada amma kuma ba shi da ilimi, sai su dinga zuwar masa da sigigin daban-daban kuma suna yi masa hidima iri-iri, k**ar kawi masa kudi da abinci da wasu abubuwa da yake bukata.mutumin da ya gamu da irin wadannan Aljanu, yawanci s**an hana shi sallah, su kan sa ya dinga dauka cewa ya zama alla (wal iyazu billah) ko ya zama Annabi. Su ma ma'abota wannan hanya cikakkun arna suke zama kuma suna samun mataslar kwakwalwa, domin a mafi yawa suna zuwa da abubuwan da mutane suke karyatawa, su kuma su dage cewa gaskiya ne.
Saidai ana iya ceto rayuwarsu ta hanyar yi musu rukiyah acire musu Aljanun, in hankalin mutum ya dawo jikinsa shikenan, sai kaga ya dena wadannan abubuwa, k**ar yadda na yiwa mutaane da yawa, mata da maza masu irin wanna aqida rukiyyah kuma an cire musu Aljanun, sun gano makaryata ne, walhamdu lillah.

To Allah Ya datar mu.
Na yi wannan bayani ne nusamman saboda wadanda suke marmarin su mallaki Aljani ya dinga yi musu aiki ko kuma suke sha'awar masu aiki da Aljanu. To ga fili nan, ga mai doki.

Rubutawar Bashir Halilu 08162600700.

Daga cibiyar Sunnah Medicine, masu yin Ruq'yah da harhada magunguna na Musulunci.

Shi ga cikin wannan shudin rubutun kayi downloading Application dinmu, wanda za ka dinga samun rubututtukanmu cikin sauki

https://appsgeyser.io/7550770/Bashir%20Halilu%20Tarbiyyah%20Islamiyyah

Lambar waya 08162600700, 08134434846

Want your practice to be the top-listed Clinic in Abuja?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address

Abuja
Other Health & Wellness Websites in Abuja (show all)
Juliet O . Gilbert Juliet O . Gilbert
Abuja

All I got right now is DREAMS�

Nycedealsng Nycedealsng
Abuja
Abuja, 900001

Nature Cares Greatly For You

HealthyEating.ng HealthyEating.ng
Abuja

Health awearness/ Health information/ Health sensitization of kids,Adults,young,old,poor,rich...

Rancy's Empire Rancy's Empire
Abuja

All kind body enhancement/weight gain,original pink lip-and scrub, feminine care products available ✅

Topform hub Topform hub
Jabi Lake Mall
Abuja, 23401

rejuvenate your health

Superlife Stem Cell STC30 Therapy Superlife Stem Cell STC30 Therapy
Behind ABC Transport Utako Abuja
Abuja

you are not made of drug so drugs can not fix you. your body is built of Cells and only STEM CELL that can fix it, because it is a live stem cell that have the capacity to maintai...

Blinkz Vitality Blinkz Vitality
Utako
Abuja, 900108

Blinkz Vitality is Expert with Top-Notch Experience in Wellness and Health Cares. Focus mostly on living a healthy lifestyle with the help of Natural/Organic Recipes. I’m looking f...

Health and wellness for all Health and wellness for all
Abuja, 14121

Whole health and wellness of supplements

Team of Therapist and Support Services for Special Needs Individuals Team of Therapist and Support Services for Special Needs Individuals
Abuja

Special Need Educators with cognate experience for all kinds of intervention.

Health and social vanguard Health and social vanguard
Jabi
Abuja, 23400

Health & Social Vanguard Incorporated is an indigenous firm vested with the responsibility of provid

Health facts Health facts
Abuja

Better health is the centeral human happiness to and well-being.vsbshh

Aksab Radio-diagnostics Aksab Radio-diagnostics
No 48 Charlotte Adesiyan, FO1 Estate, Kubwa
Abuja

Aksab is a radiodiagnostic centre, that provides diagnostic investigations, and imaging services to health centres and individuals besides clinics services we offer.